Gwamnatin Saudiyya ta bai wa Najeriya tallafin dala miliyan 10 domin yaki da masu tayar da kayar baya a kasar.
Tallafin na Saudiyya dai wani bangare ne na shirin Sarki Salman na samar da ayyukan agaji ga wadanda rikici ya shafa.
A ranar Litinin ne Ministan Tsaro na Najeriya Mansur Dan-Ali ya bayyana hakan yayin da ya tarbi tawagar Masarautar Saudiyyar a Abuja, babban birnin Najeriya.
Ministan Tsaro na Saudiyyar Mr. Nasir Mutbak ya ce an bayar da tallafin ne don samar da abinci da sauran kayan bukatu a sansanonin ‘yan gudun hijira da ke arewa maso gabashin kasar.
“Mun zo nan ne domin gabatar da sakon Sarki Salman na taimakon ‘yan uwanmu da ke sansanonin ‘yan gudun hijira a arewa maso gabas, mun zo nan ne don mu taimaka musu. Kuma tabbas mun kawo gudunmowar dala miliyan 10,” a cewar Mr Mutbak.
Minsitan Tsaron Najeriya ya tabbatar da cewa tabbas za a yi amfani da tallafin yadda ya dace wajen yaki da ta’addanci a kasar.
Gwamnatin Saudiyyar ta kuma jaddada aniyarta ta hada gwiwa da Najeriya don shawo kan matsalar tsaro da kasar ke fama da ita.
Thank's for reading my article
Saudiyya ta bai wa Nigeria dala miliyan 10 don ‘yaki da ta’addanci’Created at 2018-03-07 06:48:09
Tags:
LABARAI
0
Rate upStarShare: